Bana Nadamar Goyon Bayan Ganduje da nayi har ya Zama Gwamna – Kwankwaso

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
 Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabi’u Kwankwaso, ya ce ba ya nadamar goyon bayan Gwamna Abdullahi Ganduje har ya zama Gwamnan jihar kano.
 A lokacin da Sanata Kwankwaso yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, ya yi jawabi game da dangantakarsa da Gwamna Ganduje a baya, da kuma yadda suka yi aiki tare har zuwa 2015.
 “Ba ni da wani nadama ko kadan saboda har yanzu muna da karfi, mun fi 2015 karfi. Ba wai a Kano kadai ba har ma a fadin kasar nan da ma wajen,” in ji shi.
 An fara zaben Kwankwaso a matsayin gwamnan jihar kano a shekarar 1999 kuma an sake zabersu a shekarar 2011, inda ya cika shekaru takwas da yana mulkin jihar kamar yadda kundin tsarin mulki ya ba shi dama.
 Lokacin da Ganduje ya zama gwamna, Kwankwaso a lokacin Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya a shekarar 2015.
 Duk da cewa an zabe shi a jam’iyyar PDP, mataimakinsa na lokacin, Abdullahi Ganduje, ya gaje shi a 2015 a matsayin dan takarar jam’iyyar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta ɗaure wani ɗan Tiktok mai wanka a tsakiyar titunan Kano

    Wata kotu a jihar Kano da ke arewacin Najeriya...

Damuna: Mun shirya inganta wuraren tsayarwar motocinmu – Kungiyoyin Direbobin na Kano

Kungiyar matuka motocin kurkura ta jihar Kano da Kungiyar...

Rasuwar Aminu Ɗantata babban rashi ne ba ga Nigeria kadai ba – Mustapha Bakwana

Daga Zakaria Adam Jigirya   Tsohon Mai baiwa gwamnan Kano shawarawa...

Gwamnatin Kano ta yabawa Tinubu saboda gyarawa da bude NCC DIGITAL PARK

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin jihar Kano ta yabawa Gwamnatin...