Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta Soke Jarrabawa saboda Yajin Aikin ‘Yan adaidaita Sahu

Date:

Daga Maryam Muhd Zawaciki

Jami’ar Yusuf Maitama Sule to soke jarrabawar da za ta gudanar da karfe 8 zuwa 11 na safe a gobe Litinin biyo bayan shirin tafiya yajin aiki da matuka babun adaidaita sahu suka yi.

Kadaura24 ta rawaito wanna na kunshe cikin wata sanarwar da shugaba kwamitin shirya jarrabawar Jami’ar Dr Yau Datti ya fitar ranar Lahadin nan.

Sanarwar ta ce kwamitin zai tuntubi shugaban Jami’ar domin yanke hukunci kan makomar sauran jarrabawar da za a rubuta.

Tun kwanaki uku da suka wuce yan Sahun suka raba takardun Kira ga matukan da su shiga yajin aikin mako guda don nuna adawarsu ga sabunta koriyar lamba da hukumar KAROTA ta ce suyi.

Haka kuma tun da yammacin yau Lahadi aka ga sun fara sanya ganye alamar yajin aikin na man daram babu gudu babu ja da baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...