Gwamnatin Taliban Za ta Fara Zane Waɗanda Su Ka Je Masallacin Juma’a a Makare a Kasar Afghanistan

Date:

 

Gwamnatin Taliban, a ƙasar Afghanistan ta sanar da wata sabuwar doka da ta shafi dukkan al’ummar kasar.

Dokar ta baiyana cewar, da ga yanzu duk wanda ya makara bai je masallacin Juma’a ba har a ka fara Huɗuba, to za a yi masa bulala 25.

Dokar ta ce hukuncin babu babba, babu yaro, in da gwamnatin ta ce “saboda haka hukumomin Gwamnatin Taliban su ke kira ga dukkan al’ummar ƙasar Afghanistan da su kiyaye wannan doka, wajen zuwa Masallacin Juma’a akan kari.”

Daily Nigerian ta rawaito Gwamnatin ta baiyana cewar dokar za ta fara ne daga gobe Juma’a, shi ya sa ma a ka shiga kasuwanni ana sanar da jama’a dokar a yau.

A gefe guda kuma, Gwamnatin ta samar da isassun bulalai ga dukkan jami’an tsaro da za su bi layi-layo don hukunta masu kunnen ƙashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...