Ba da Wanda Muke Maganar Zan Koma APC – Sanata Kwankwaso

Date:

Daga Nura Abubakar Darma

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa bashi da Wani Shiri na barin jam’iyyar sa ta PDP Zuwa Jam’iyyar APC Mai Mulkin Nigeria.
Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne Cikin Wata Hira da yayi da Gidan Radio na DW dake Kasar Jamus.
Gidan Radio ya rawaito Sanata Kwankwaso ya na cewa a Yanzu dai bashi da Wata niyya ta barin jam’iyyar PDP Zuwa APC Kamar yadda ake ta jita-jitar zai bar jam’iyyar Saboda Rashin Yi da shi da ba a yi a jam’iyyar.
Maganar sauya Sheka Babu ita a yanzu din nan, bana Magana da Wasu Mutane Kan cewar Zan Koma APC” inji Kwankwaso
“Amsar da tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayar dangane da jita-jitar da ake yadawa kan cewa zai sauya sheka daga babbar jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC”. Gidan Radio ya rawaito
Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Cewa an Fara tunani Kwankwaso da Ganduje zasu yi Sulhu ne tun bayan da Gwamna Ganduje ya Kaiwa Sanata Kwankwason Ziyarar ta’aziyyar kaninsa da ya rasu a kwanakin baya.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Dalilin da ya hana Sarki Aminu Ado Bayero zuwa gidan yari na goron dutse a yau alhamis

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin...

Matakai 3 da gwamnatin Kano ta dauka kan kafafen yada labarai a jihar

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta ce a...

Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Daga Umar Ibrahim kyarana   Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar...