Kanywood ta Barranta Kanta da Wani Shirin fim Mai Suna Makaranta wanda a ciki batun Jima’i

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

Shugaban Jarumai masana’antar Kanywood Alhassan Kwalle ya barranta masana’antar su ta Kanywood da Wani Shirin fim da Yanzu haka ake tallansa a YouTube.
Alhassan Kwalle ya bayyana hakan ne yayin wata Ganawa da yayi da Wakilinn Kadaura24 a Ofishin sa.
Alhassan Kwalle yace Shirin da ake tallafan ya sabawa koyarwa ta addinin Musulci da al’adun Hausawa da kuma dokokin masana’antar don haka suke barranta kansu da fim din.
Shugaban Jaruman ya Kuma ce zasu tabbatar da Cewa zasu dauki matakan da suka dace na shari’a akan Wanda ya Shirya fim din ,duk da mashiryin Shirin ba don masana’antar ba ne.
“Mun yi waya da mashiryin Shirin domin in Sanar da Shiri cewa abun da sukai ba dai-dai bane, Amma tun a tashin fari yace shi fa ba dan Kanywood bane, ya Shirya Shirin ne a karan Kansa”. Inji Alhassan Kwalle
Kwalle ya ce yana da yakinin Hukumar tace Fina-finan ta Jihar Kano bazata bar abun sakakaba, yasan zata dauki Matakin daya dace domin hana Fitar da fim din don gudun lalata tarbiyyar al’umma.
A Jawabinsa Shugaban Hukumar tace Fina-finan Hausa ta Jihar Kano Isma’ila Na-Abba afakallah yace zasu lamunci irin badala a Cikin Fina-finai ba , Inda ya bayar da tabbacin Hukumar zata lalubo Mashiryin Shirin domin gurfanar da shi a gaban shari’a.
Yayin Zantawarsa da Manema labarai Afakallah yace Aikin Hukumar ne ta hana yin fim din da ya sabawa addinin Musulci da al’adun Malam Bahaushe a don tabbatar da sauke nauyin da Gwamnati ta dora Mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba gaskiya a bayanin wasu Manoman Kano da suka ce Muna karbar kudi a wajensu – Civil defense

Rundunar tsaro ta Civil defense ta Kasa reshen jihar...

Korar ma’aikata a Kano: Bashir Gentile ya yiwa Faizu Alfindiki martani mai zafi

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Masanin kimiyar siyasa kuma mai sharhi...

Sakataren kungiyar NRO Abdulkadir Gude ya rasu

Allah ya yi wa dattijo, kuma Sakataren kungiyar Northern...

Gwamnatin da ta ke korar Ma’aikata ba ta Cancanci Wa’adi na biyu ba – Faizu Alfindiki

Daga  Maryam Muhammad Ibrahim   Abin takaici ne ganin yadda gwamnatin...