Gwamnonin APC Ga Jonathan: Kada a Yaudare ka ka bar PDP don Samun Tikitin Takarar Shugaban Kasa a APC 2023

Date:

Daga Umar Hussain Mai Hula
 Gabanin zaben shugaban kasa na 2023, ana ta yada jita-jitar cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari yana zawarcin tsohon shugaban kasa, Dr. Goodluck Jonathan a sirrance don ya dawo zuwa jam’iyyar APC.
 Sai dai kungiyar gwamnonin jam’iyyar APC, ta gargadi tsohon shugaban kasa Jonathan da kada ya bari a shawo kansa ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC da nufin tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.
 Sun tabbatar da cewa wannan matakin zai yi tasiri sosai wajen rage masa kima a matsayinsa na dattijo
 Darakta Janar na PDF, Salihu Lukman wanda ya bayyana hakan a kan koma bayan da ake ta rade-radin cewa Jonathan Zai koma APC, ya ce kada jam’iyyar ta bar tsohon shugaban kasar ya rage Mata kima ta hanyar tsayar da shi takara a kowane zabe a Najeriya.
 Sun yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika tattauna Kan abun da zai taimake ya taimaki shugabanninsu.
 Idan dai za a iya tunawa, Jonathan ya amince da shan kaye tun kafin a bayyana sakamakon zaben shugaban kasa na 2015 a hukumance ba;  Wanda hakan yasa ya samu karbuwa a kasa da ma duniya baki daya.
 Bayan wasu ‘yan watanni ana ta cece kuce a tsakanin su, musamman kan yadda aka Zargi PDP ta karkatar da kuɗin al’umma a lokacin da take mulki, Buhari ya rika nunawa kamar sun yi sulhu da Jonathan.
 Jagororin biyu sun kasance suna ganawar Sirri akai-akai a fadar Aso Rock Villa.
 Duk da dai har yanzu Jonathan bai yi magana kan rade-radin da ake yi masa na yin na komawa da jam’iyyar APC ba, amma shugabannin Kudancin kasar sun bi sahunsa wajen ba shi shawarar Kar ya sake ya dauki wannan matakin

1 COMMENT

  1. Its like you read my mind! You seem to know so much about this,
    like you wrote the book in it or something. I think that you can do with a few pics to drive the
    message home a little bit, but instead of that, this is great blog.
    A great read. I will certainly be back.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...