Inganta tsaro: Gwamnan Kano ba da kyauatar Motoci da babura ga Rundunar Hadin gwiwa

Date:

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya yaba wa rundunar sojin Najeriya bisa gaggawar da ta yi wajen dakile hare-haren ’yan bindiga da aka samu a wasu sassan jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24.

InShot 20250309 102512486

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi babban kwamandan Runduna ta 1, Manjo Janar Abubakar Sadiq Muhammad Wase a gidan gwamnati.

Janar Wase, wanda ya ce ya je Shanono da Tsanyawa, domin duba yanayin tsaro a yankin, ya fadawa gwamnan cewa ya tuna da lokacin da mahaifinsa marigayi Kanar Muhammad Abdullahi Wase ya jagoranci jihar a 1994.

Ya ba da tabbacin zai yi aiki tukuru domin gance duk wata barazanar tsaro dake tasowa a wasu sassa na jihar Kano.

China ta mayar wa Amurka martani kan barazanar hari da ta yi wa Nijeriya

Da yake jawabin Gwamna Yusuf ya gode wa jami’an tsaro bisa jajircewarsu, tare da mika godiya ga Shugaba Bola Tinubu bisa nadin manyan hafsoshin tsaro da ya ce suna aiki tukuru.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati ta ba da motoci Hilux 10 da babura 60 ga rundunar hadin gwiwa da ke aiki a yankunan da abin ya shafa, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro wajen yaki da ’yan bindiga, garkuwa da mutane da kuma satar shanu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...