Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Date:

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce zai ci gaba da harkokin siyasa har zuwa lokacin da zai bar duniya.

Malam Shekarau ya bayyana hakan ne yayain taron manema labarai da ya kira a gidan sa a wani bangare na bikin cikar sa shekaru 70 da haihuwa.

InShot 20250309 102512486

Shekarau ya ce wajibi ne ɗan adam ya shiga harkar siyasa don kawo canji mai kyau.

A cewar Shekarau, shiga siyasa lamari ne da zai baiwa dan adam dama ya bada gudunmawar da wajen taimakawa al’umma, inda ya ce burin da a duniya shine taimakon al’umma.

Shekarau ya kara da cewa ya kamata dai mutum ya shiga siyasa da kyakkyawar niyya, inda ya ce shi ya sha fada cewa ya na kula da addinin sa na Musulunci a harkokin siyasar sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...