China ta mayar wa Amurka martani kan barazanar hari da ta yi wa Nijeriya

Date:

Gwamnatin kasar China ta fitar da gargadi mai karfi kan duk wani yunkuri na tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Najeriya, bayan kalaman da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na barazanar kai hari da sojoji a Najeriya bisa zargin cin zarafin Kiristoci.

Da take jawabi a wajen taron manema labarai a ranar Talata, Mao Ning, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar China, ta bayyana cewa, Beijing “na goyon bayan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu gaba ɗaya yayin da take jagorantar al’ummar Najeriya kan tafarkin ci gaba da ya dace da halin ƙasar.”

InShot 20250309 102512486

“China, a matsayinta na abokiyar haɗin gwiwar Najeriya, tana adawa da duk wata ƙasa da ke amfani da addini ko kare haƙƙin ɗan adam a matsayin hujja don tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wata ƙasa ko yin barazanar sanya mata takunkumi ko amfani da ƙarfi,” in ji Mao.

Wadannan kalamai sun biyo bayan martanin ƙasashen duniya kan maganganun Trump da ke haifar da damuwa a diflomasiyya a fadin nahiyar Afirka da ma sauran sassan duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...