Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nigeria ta karyata zargin kwace fasfo din Sanata Natasha a Filin Jirgi

Date:


‎Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya ta musanta zargin da Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta yi cewa jami’anta sun hana ta tafiya tare da karɓe mata fasfo dinta a filin jirgi.

‎Mai magana da yawun hukumar, Akinsola Akinlabi, ne ya bayyana hakan ga gidan Talabijin na Channels a ranar Talata .

‎Ya bayyana cewa abin da ya faru kawai tsarin binciken shige da fice ne da ake gudanarwa ga kowane fasinja.

InShot 20250309 102512486

‎A cewar Akinlabi, “Hukumarsu ba ta karɓe fasfo din sanata Natasha ba. bincike nna shige da ficen da ake yi ga kowa, sannan aka amince ma ta ta yi tafiyarta.”

‎Ya ƙara da cewa jami’an hukumar suna yin aikinsu ne bisa ka’ida, kuma yuwuwar karbar fasfo na ɗan lokaci domin tantancewa ba yana nufin an kwace shi gaba daya.

China ta mayar wa Amurka martani kan barazanar hari da ta yi wa Nijeriya

‎“Jami’anmu dole ne su aiwatar da binciken su. Suna iya karbar fasfo domin duba bayanai, amma hakan ba yana nufin kwacewa ba. Bayan an kammala bincike an bar ta ta tafi,” in ji shi.

‎Hukumar ta kuma ce sanatar ta yi bidiyon korafinta ne a lokacin da ake gudanar da binciken, kuma tuni an bar ta ta wuce domin tafiya inda ta ke so.

‎Da aka tambaye shi ko sanatar ta ƙi mika fasfon nata domin duba shi, mai magana da yawun ya ce ba shi da tabbacin hakan.

‎“Ban san wannan ba. Amma jami’anmu suna da hurumin karɓar fasfo domin tantancewa, sannan su mayar bayan sun gama kuma haka suka yi,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...