An kaddamar da Sabbin Shugabanin kungiyar Masu Zurga-zurgar sufiri a Jihar Kano

Date:

Daga Kabiru Muhd Getso

Kwamishinan Aiyuka na jihar Kano Engr Idris wada ya kaddamar da kungiyar zurgazurgar Sufuri reshe jihar kano tare da bude masu sabon ofishi a harabar ma’aikatar ayyuka.

Engr idris wada ya bayyana cewa sufuri na da matukar muhimmanci ga rayuwar al’umma hakan tasa Gwamnatin jihar kano karkashin Shugabancin Dr Abdullahi Umar Ganduje a shirye suke domin bada gudummuwar da duk ya kamata don ha6aka sufuri a jihar Kano.

Shi ma a nasa jawabin sabon Shugaban Masu Zurga-zurgar ababan hawa na jihar kano Alh Lawan Isah Bubaram ya bayyan gansuwarsa akan yadda Gwamnati ke bada kulawa ta musamman akan harkar sufuri a kano, Sannan ya yi Kira ga sauran al’umma da su cigaba da bada cikakken hadin Kai akan sha’anin Sufuri.

Lawan Isah Baburam ya sha alwashin bin matakan da duk ya kamata domin ciyar da wannan kungiya gaba, tare da bijiro sabbun dabaru domin farfado da kungiyar tayi gogayya da sauran takwarorinta na jihoshi.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...