Kungiyar tsofin sojoji sun gudnar da zanga zangr lumana

Date:

Saminu Ibrahim magashi

Gamayyar kungiyar tsofaffin sojojin dake fadin kasar nan  sun gudanar da zanga zangar lumana, Sakamakon  rashin biyansu wasu hakkoki da suka ce Gwamnatin tarayan ta gaza .

Zanga-zangar da Gamayyar ta hadar da Kungiyar tsofafin Sojojin Sama, da Sojojin Ruwa, da kuma Sojojin Kasa. suka gudanar .

Masu zanga-zangar sun zagaya wasu muhimman gurare da suka hadar da Gidan gwamnati da Gidan sarki. Harma ya yin zuwansu gidan sarkin suka sami Wakilin Sarki Alhaji Mahe Bashir Wali ya tarbe shu a madadin Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayaro.

A jawabin Kodinetan Kungiyar a matakin jiha, Junaidu Umar ya bayyana cewa sun fito wannan zanga zanga ta Limana Sakamakon gazawar da Gwamnatin Tarayya ta yi na Kasa biyan su hakkokin su yasa suka fito don nuna damuwar su ga Mahukunta.

Mun hidimtawa Ƙasar nan tun Muna da karfin mu tsahon shekaru 35 Amma har Yanzu hakkokin mu sun makale ,Kuma hakan yasa da yawa daga cikinmu shiga halin kakanikayi “ini Junaidu Umar

A karshe tsofafin sojojin na fatan Gwamnatin da tarayya da sauran masu ruwa da tsaki dasu tallafa danganin ancire musu hakkokin nasu.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...