Kada Ka Rudar da Tarihi, Ba Ka Cikin Wadanda Suka Kafa APC – Alfindiki Ya Fadawa Kwankwaso

Date:

Jigo a jam’iyyar APCn kano kuma babban mai taimaka wa Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Faizu Alfindiki, ya musanta ikirarin da tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi na cewa yana daga cikin wadanda suka kafa jam’iyyar APC.

Faizu Alfindiki ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24 a ranar Asabar. Ya bayyana cewa babu wata shaida a tarihi da ke nuna cewa Kwankwaso ya na cikin wadanda suka taka rawar gani wajen kafa jam’iyyar, domin kuwa ba ya cikin jam’iyyun da suka hadu wajen samar da APC a shekarar 2013.

Ya ce jam’iyyun da suka dunkule suka kafa APC sun hada da CPC karkashin marigayi Janar Muhammadu Buhari, da ACN karkashin jagorancin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, APGA karkashin Sanata Rochas Okorocha, da kuma ANPP karkashin Kashim Shettima, marigayi Bukar Abba Ibrahim, Malam Ibrahim Shekarau da Yariman Bakura.

Rundunar yansanda ta Kano ta kama wasu da suna yi fashi da makami a Lagos

Alfindiki ya kuma bayyana cewa wasu fitattun ‘yan siyasa kamar Rotimi Amaechi, Aliyu Wamakko, Murtala Nyako da Bukola Saraki ne suka shiga jam’iyyar daga baya a 2014, shekara guda bayan kafa ta.

FB IMG 1753738820016
Talla

Duk da haka, ya amince da cewa shigar Kwankwaso cikin jam’iyyar ya taimaka mata a zaben 2015, inda ya samu kujerar Sanata, mataimakinsa ya zama gwamna, sannan APC ta lashe dukkanin kujerun yan majalisar tarayya dana jihar Kano.

Alfindiki ya ce kamata ya yi Kwankwaso Sai ya ci gaba da godewa jam’iyyar APC domin ita ce ta farfado da siyasar sa a lokacin da ta ke dab da rushewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda Dansanda ya harbe kansa da bindiga a Kano

Wani jami’in dansanda mai suna Aminu Ibrahim ya rasa...

Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince...

Kudade: Ganduje ya caccaki Gwamnatin kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Tsohon shugaban jam’iyyar APC...

Gwamnan Kano ya tura sunayen mutane biyu majalisar dokokin don nada su a mukaman Kwamishinoni

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mika...