Rundunar yansanda ta Kano ta kama wasu da suna yi fashi da makami a Lagos

Date:

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta bayyana samun gagarumar nasara a binciken da ta gudanar kan wani mummunan harin fashi da makami da kuma yunƙurin kisa da ya faru a Bera Estate, Chevron, Legas.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya aikowa Kadaura24, dakaru Rundunar na musamman ne suka cafke wasu mutane biyu da ake zargi da hannu a lamarin a ranar 11 ga Satumba, 2025 a unguwar Na’ibawa, Kano.

Wadanda aka kama sun haɗa da:

Mathew Adewole, mai shekaru 25 daga Na’ibawa Quarters, Kano.

Mukhtar Muhammad, mai shekaru 31 daga Unguwa Uku Quarters, Kano.

Mathew Adewole ya amsa cewa shi ne ya kai hari kan wani mazaunin Bera Estate mai suna Lil-Kesh a ranar 19 ga Agusta, 2025. Ya yi masa mummunan rauni a wuya, a kokarinsa na yin fashi da kuma kisa.

Ya tilasta wa wanda aka kai wa harin ya tura naira miliyan 2 da dubu 120 (₦2,120,000) daga asusunsa ta wayar salula zuwa asusun Mukhtar Muhammad.

A cewar sanarwar, rundunar ta bi umarnin babban sifetan ‘yan sanda na kasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, wajen ƙara ƙarfin masu leken asirinta da kuma haɗa gwiwa jama’a domin dakile miyagun laifuka.

FB IMG 1753738820016
Talla

An mika waɗanda ake zargin ga rundunar ‘yan sanda ta Jihar Legas domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da su a gaban kuliya.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori ya yaba da ƙoƙarin jami’ansa da kuma haɗin kan jama’a, tare da tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aiki tukuru wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...