Ziyarar Aiki: Shugaba Tinubu Ya Iso Lagos

Date:

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya isa birnin Lagos a ranar Juma’a domin ziyarar aiki , yayin da Najeriya ke shirin bikin cikar ta shekaru 65 da samun ‘yancin kai a cikin salo na takaita bikin

Shugaban Ƙasan ya je Lagos ne bayan halartar bikin nadin Sarkin Ibadan, Oba Rashidi Ladoja, a tsohon birnin Ibadan dake jihar Oyo.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Kasar Bayo Onanuga ya fitar .

Yace a yayin zamansa a Lagos, Shugaba Tinubu zai gana da manyan ‘yan kasuwa na ƙasar da kuma jami’an gwamnati na matakin koli.

Kazalika, a ranar Talata 30 ga Satumba, Shugaban Ƙasan zai ziyarci jihar Imo domin kaddamar da wasu muhimman ayyuka da Gwamna Hope Uzodimma ya aiwatar.

A cikin shagulgulan bikin ‘yancin kai, Shugaba Tinubu zai kuma kaddamar da sabuwar cibiyar al’adu da fasaha wadda aka chanza mata suna zuwa Cibiyar Wole Soyinka ta Al’adu da Fasaha.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...