Ganduje ya tafi Kasar Amurka, ya mika mulki ga Gawuna

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
 Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya tafi kasar Amurka inda yake halartar wani shiri na tsawon mako Guda akan jagoranci.
  KADAURA24 ta rawaito Sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa Gwamna Ganduje na halartar wani shiri na inganta jagoranci na kwarai a makarantar kasuwanci ta Harvard da ke Boston.
 Ya ce gwamnan ya mika mulki kuma ya ba mataimakin gwamna Dakta Nasir Yusuf Gawuna cikakkiyar damar zama mukaddashin gwamnan jihar.
 Sanarwar ta kara da cewa duk wata harkokin mulki daga yanzu sai an bi ta ofishin mataimakin gwamna domin daukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...