Babbar Sallah : Kansilan Lajawa ya raba Naira dubu 500 ga al’ummar mazabarsa

Date:

Daga Nura Adam

 

Kansilan mazabar Lajawa a karamar hukumar Wudil ta jihar Kano Hon. Muttaka Lawan ya rabawa mutane sama da 100 a mazabarsa kimanin Kudi Naira dubu Dari Biyar domin su gudanar da shagulgulan sallah Babba.

Da yake jawabi a wajen taron Hon. Muttaka A Lawan ya ce ya raba kudaden ne domin al’ummarsa su sami damar gudanar da bukukuwan babbar Sallah cikin nutsuwa.

IMG 20250415 WA0003
Talla

” Mun kawo wannan abun alkhairin ne a wannan lokaci da mu ka san cewa al’umma suna cikin wani hali, don haka muke fatan za ku yi hakuri da dan abun da mu ka samu har mu ka kawo muku”. Inji Hon. Muttaka Lawan

Dama ba mu yi shirin yin hawan babbar Sallah ba – Sarki Aminu Ado Bayero ya fadi dalili

Ya ce wannan somin tabi ne, nan gaba zai cigaba da yin duk mai yiwuwa don tabbatar da ganin al’ummar mazabar Lajawa sun cigaba da sharbar romon dimokaradiyya.

An dai raba kudaden ne ga rukunonin mutane daban-daban kamar haka :

1. NNPP OPTION A

2. NNPP OPTION B

3. SOCIAL MEDIA

4. 5000 FOR 25 PEOPLE

5. KUNGIYAR MATA

6. KUNGIYAR DATTIJAI

7. 2000 FOR 20 PEOPLE

8. SAURAN YAN JAM’IYYA

InShot 20250309 102403344

Wasu daga cikin wadanda su ka amfana da tallafin sun yabawa kansilan tare da yin kira ga sauran Kansilolin da masu mukaman Siyasa da su yi koyi da Hon. Muttaka A Lawan wajen taimakawa yan jam’iyya da sauran al’ummar garin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...