Karyewar Gada: Matafiya na Fuskantar Barazana a kan Iyakar Kano da Jigawa

Date:

Daga Kabir Muhd Getso
Al’umma da dama na kokawa bisa karyewar wata gada da ke iyakar Jihar kano da jigawa.
Wani matafiyi da Wakilin Kadaura24 ya zantawa da shi ya shaida masa cewar matafiya na shan bakar wahala a sakamakon lalacewar gadar, inda ta kai dole sai dai a gangara ta kasan gadar  abi ta cikin ruwa domin tsallakawa Wanda hakan kan haifar da lalecewar ababan hawa da dama.
Wasu mazauna yankin sun bayyana wahalar da matafiya ke sha a kokarin tsallaka wannan gada, sun kara da cewar tun kafin ta gagara hawa sunyi kira ga mahukunta amma ba’a samu nasarar kawo mata dauki ba. Don haka suke kira ga mahunta da su dauki kwakkwaran mataki akan wannan gada.
Shi ma shugaban karamar hukumar Birnin kudu dake Jihar Jigawa Hon Magaji Yusuf Gigo ya bayyana mana cewar duk da cewar wannan aiki na Gwamnatin tarayyar ne za su bi duk matakin da ya kamata wajen tuntubar ‘yan majalisu domin samun gudanar da wannan aiki cikin gaggawa.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Daga Isa Ahmad Getso ‎ ‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers ta bayyana...

Rahoto: An kwantar da Buhari a ICU a Landan

  Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin...

Kacibus: A karon farko an hadu tsakanin Gwamnan Abba da Sarki Aminu Ado a Madina

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   A karon farko an hadu tsakanin...

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...