Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Date:

Daga Ibrahim Abubakar Diso

 

Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya wakilci karamar hukumar Gwale Muhammad Bashir Hussari Galadanchi ya raba kudi da shanu ga Shugabannin jam’iyyar APC na Karamar hukumar .

Hon. Muhammad Bashir Hussari Galadanchi ya gwangwaje yan jam’iyyar APC da shanu har goma sha daya inda kowacce mazaba za ta rabauta da sa guda daya.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Su kuma shugabannin jam’iyya na karamar hukumar Gwale an ba su sa guda daya .

Haka zalika Hon. Hussari ya baiwa dattijan jam’iyya Naira miliyan daya da Dubu Dari shida (1.6), tsohon dan majalisar ya kuma ba da Naira dubu uku-uku ga yan jam’iyyar APC dubu uku dake karamar hukumar Gwale.

Kungiyar RATTAWU ta aike da ta’aziyyar mutane 22 yan wasan Kano da suka rasu

Kazalika Hon. Hussari ya rabawa yan social media na karamar hukumar Gwale dubu shida-shida .

Husari ya raba shanu Goma sha daya, inda kowanne shugaban APC na mazabun 11 za su sami guda.

InShot 20250309 102403344

Da yake bayyana sakon tsohon dan majalisar, shugaban jam’iyyar APC na Karamar hukumar Gwale Umar Yusuf Kashekwabo ya ce Hussari ya ba da tallafin ne domin tallafawa yan jam’iyyar don su yi bikin Sallah cikin nishadi.

 

” Muna yabawa wannan Hon. Hussari bisa Wannan kokarin da ya yi, kuma hakan ya nuna yana kimanta Shugabannin jam’iyyar APC, saboda cewa ya yi Shugabannin jam’iyyar yake so su raba kayan don su Isa ga wadanda ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...