Kotu ta ce Hana Muhd Sanusi II shigowa Kano ya sabawa doka

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Talatar nan, ta umurci gwamnatin jihar Kano da ta Nemi afuwar tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II a wasu jaridun kasar guda biyu.
 Kotun, a wani hukunci da mai shari’a Anwuli Chikere ya yanke, ta ce korar Sanusi daga kan karagar mulki sarautar Kano ya sabawa ka’ida, kuma ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar, kuma ya yi matukar tauye hakkinsa na dan Adam.
 Don haka, ta Umarci Gwamnatin Kanon ta baiwa Sanusin diyyar  Naira miliyan 10,
 Yayin da yake gabatar da takaitaccen bayani na karshe, lauyan Sanusi, Abubakar Mahmoud, SAN, ya shaida wa kotun cewa wanda yake karewa ba kalubalantar tsige shi.
 Mahmoud ya ce wanda yake karewa ya Kawo kara gaban kotu kan yadda ake tauye masa hakki dangane da aka yi masa bayan da gwamnatin jihar Kano ta tsige shi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...