Yadda Rikici ya barke tsakanin yansanda da mutanen gari a Kano

Date:

Rahotanni daga Karama hukumar Rano dake jihar Kano a Nigeria na tabbatar da cewa a yau ne wani rikici ya ɓarke a karamar hukumar biyo bayan zargin mutuwar wani matashi mai suna Abdullahi Musa a hannun ‘yan sanda yayin da ake tuhumarsa.

An dai tuhumi matashi ne da laifin saɓa dokar hanya, lamarin da ya janyo ƴansanda su ka tsare shi, wanda hakan ya janyo zanga zanga a garin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Yanzu haka dai zanga-zangar ta rikide zuwa tashin hankali a lokacin da masu zanga-zangar suka cinna wa ofishin ‘yan sanda wuta.

Gwamnatin Kano ta kama na’urorin da ake buga hotunan batsa

Shaidun gani da ido sun ce lamarin ya ta’azzara ne bayan da aka ce ‘yan sanda sun bude wuta kan masu zanga-zangar, inda wasu matasa biyu suka jikkata.

Hakan tasa matasan garin suka kone ofishin yansandan tare da jikkata DPO.

InShot 20250309 102403344

Kadaura24 ta rawaito da yake tsokaci kan faruwar lamarin, Jami’in hulda da jama’a na rundunar yansanda ta kasa reshen jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce za su gudanar da bincike tare da daukar matakan da suka dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...