Inganta ilimi: Shugaban Karamar hukumar Ungoggo ya kaddamar da rabon kayan koyo da koyarwar

Date:

Daga Shehu Usaini Getso

Shugaban karamar hukumar Ungoggo Alhaji Tijjani Amiru Bilyaminu ya kaddamar da rabon Kayayyakin Koyo Da koyo don bunkasa Ilimi a yankin

Shugaban karamar hukumar Ungogo, Alhaji Tijjani Amiru Bilyaminu ne ya jagoranci kaddamar da rabon kayayyakin koyo da koyarwa a cibiyar yada addinin musulunci da ke yankin.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Alhaji Tijjani Amiru Bilyaminu ya bayyana cewa an samar da kayayyakin ne domin tallafawa ci gaban karatun dalibai.

Ya kuma mika godiyarsa ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa wajen aiwatar da duk abun da zai bunkasa ilimi a Kano.

Karyewar gada ya jefa dubban al’umma cikin mawuyacin hali a Rano, Sun nemi Agajin Gwamnan Kano

A nasu jawabin sakatariyar ilimi ta karamar hukumar Hajiya Hussaina Ibrahim da kansilan ilimi Abdullahi Wakili sun tabbatar da cewa makarantun yankin sun karbi kayayyakin koyo da koyarwa tare da kayan shakatawa na zamani.

A nasa jawabin shugaban kwamitin ilimi na karamar hukumar, Alhaji Sammani Muhammad Zango ya bukaci malamai da su yi amfani da kayan tare da ci gaba da aiki tukuru domin bunkasa ilimi.

InShot 20250309 102403344

A wata sanarwa da jami’in yada labaran yankin Salisu Kassim Yakasai ya aikowa Kadaura24, ya ce wasu daga cikin shugabannin makarantu a yankin, Malam Isa Amunu da Malama Binta, sun tabbatar da aniyarsu ta yin amfani da kayan koyarwa da aka tanada yadda ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...