Hajjin Bana: An sanya ranar da Alhazan Kano za su fara tashi zuwa Saudiyya

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta ce Maniyatan jihar za su Fara tashi zuwa kasa mai tsarki domin sauke farali a bana a ranar 13 ga watan mayun shekara ta 2025.

Shugaban Hukumar Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya bayyana hakan a yau yayin wata ziyara da ya kai cibiyoyin karatun koyon Aikin Hajj na kananan hukumomin Ungogo da Bichi, a wani bangare na shirin Hajjin shekarar 2025.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Sulaiman Abdullahi Dederi ya aikowa Kadaura24 ranar asabar.

Sanarwar ta ce Alhaji Lamin Rabi’u ya bayyana cewa, bisa ga jadawalin da Hukumar kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta fitar, cewa Jihar Kano za ta fara jigilar alhazanta zuwa Saudiyya tare da kamfanin jirgin sama na Max Air a ranar 13 ga Mayu, 2025.

Hajjin bana: Saudiyya ta fitar da jerin Harsuna 20 da za a fassara hudubar Arfat da su

Ya kara da cewa Hukumar ta kammala dukkan shirye-shiryen da suka kamata tun da wuri, domin tabbatar da cewa an gudanar da jigilar alhazan cikin nasara da tsari.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar, Alhaji Yusif Lawan, ya ja hankalin mahajjata masu niyyar tafiya da su rika halartar karatun koyon Aikin Hajji a kai a kai domin amfanin kansu.

InShot 20250309 102403344

Haka kuma, ya gargade su da su kiyaye bin dokoki da ka’idojin na hukumomin Najeriya dana wadanda Saudiyya suka shimfiɗa domin tafiyar da aikin Hajji.

Shugaban Hukumar tare da dukkan mambobin kwamitin da daraktoci sun halarci wannan ziyarar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...