Da dumi-dumi: NNPC zai raba man fetur kyauta

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kamfanin albarkatun mai na Nigeria NNPC ya sanar da fara bayar da man fetur kyauta ga masu ababen hawa a babban birnin tarayya Abuja da kuma jihar Bauchi.

A wata sanarwa da kamfanin ya aikowa Kadaura24, ya ce kamfanin zai raba man ne kyauta a wasu sabbin gidajen mai mallakin kamfanin da aka bude a Abuja da Jihar Bauchi.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Sanarwar ta ce ” NNPC ya sake bude sabbin gidajen man ne a kokarinsa na ganin ya saukakawa yan Nigeria sun sami man fetur cikin sauki kuma a kusa da su.

Gwamnatin Kano, za ta kula alakar Noma, kasuwanci da makamashi da kasar Morocco

” Za mu bayar da man ne ga masu motoci da babura, domin nuna godiya ga al’umma bisa irin hadin kan da suke ba mu a ko da yaushe”.

InShot 20250309 102403344

” A Abuja kan titin Airport Road za mu baiwa masu babura kimanin 200 lita 5 – 5 na man fetur kyauta, yayin da kuma a sabon gidan man NNPC dake Kano – Ningi Road mu ka riga muka bayar da kyautar man ga kwastomomi da suka fara zuwa sayan mai a wurin mu a ranar 17, ga watan Afirilun 2025″.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...