NBC ta haramtawa Gidajen Radio da TV sanya wakar da Eeedris Abdulkarim ya yiwa Tinubu

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

Hukumar kula da kafafen yada labaran na Radio da talabijin ta Kasa NBC ta haramtawa gidajen rediyo da Talabijin na Najeriya sanya wata waka mai suna “Tell Your Papa” wadda fitaccen mawakin nan, Eeedris Abdulkareem ya rera.

Sanarwar da NBC ta fitar ta ce wakar ta yi nuni sosai don haka dole wakar ta zama abar kyama .

A cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan Afrilu 9, 2025, wadda shugabar hukumar ta NBC Susan Obi, ta fitar, ta bayyana cewa hukumar ta ayyana wakar a matsayin wakar da bata dace a sakata a gidajen radio da talabijin ba saboda ta sabawa sashe na 3.1.8 na dokar yada labarai ta Najeriya.

FB IMG 1744283415267
Talla

Wannan sashe ya hana ya duk wasu abubuwan da ake ganin ba su dace ba, kamar zagi, keta mutuncin jama’a a gidajen radio da talabijin a Najeriya.

Damina: Gwamnati ta bayyana jihohin da za su iya fuskantar ambaliyar ruwa a Nigeria

A cewar NBC, waƙar ta sami karbuwa a dandalin sada zumunta, abubuwan da ke cikin waƙar ta sun karya ka’idojin hukumar .

InShot 20250309 102403344

NBC ta haramta sanya wakar Eedris Abdulkareem mai suna “Tell your Papa” don haka ta gargadi duk kafafen yada labarai na radio da talabijin a fadin Nigeria da su guji yada wakar.

A cikin waƙar dai Mawakin ya soke shugaban kasa Tinubu ta hanyar aika sako ga Shugaban kasar ta hannun dansa Seyi Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar samarin Tijjaniyya ta yi Allah – wadai da hukuncin Kotun ECOWAS

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Kungiyar Samarin Tijjaniya ta kasa tace...

Majalisar dokokin Kano da Freedom Radio sun fara musayar kalamai

Majalisar dokokin jihar Kano ta nemi al'ummar jihar Kano...

2027: Shugabannin APC a Kano ta Kudu sun mika bukatarsu ga Sanata Kawu Sumaila

Shuwagabannin jam’iyyar APC da Sakatarorin su na mazabar Kano...

Tinubu ya sake ƙaddamar da aiki titin Abuja zuwa Kaduna

Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da aikin sake gina...