INEC ta karbi takardar neman yi wa Sanata Natasha kiranye

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa ta karɓi ƙorafi da ke neman fara yunƙurin yi wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kiranye a matsayin Sanata.

Sakataren hukumar, Rose Oriaran-Anthony ce, ta karɓi ƙorafin a yau Litinin.

InShot 20250309 102403344
Talla

Ƴan mazaɓar, a wata wasika da jagoran su, Salihu Habib ya sanyawa hannu, sun nuna cewa sun dawo daga rakiyar wakilcin Natasha a majalisar dattawa.

Masu korafin, karkashin ƙungiyar Concerned Kogi Youth and Women, sun yi kira ga INEC da ta gaggauta sahale yunƙurin kiranyen, wanda su ka ce hakan hakan na da kyau wajen karfafa dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Sarki Aminu Ado Bayero ya fara daukar matakan gudanar da Hawan Sallah Karama a Kano

Hakan ya zo ne bayan da tun a farko, kotu ta hana INEC karɓar korafi na yunkurin yi wa Natasha kiranye, amma kuma wanne tudu wanne gangare, sai kotun a yau Litinin ta baiwa hukumar zaben damar karbar korafe-korafen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...