Matsalar Albashi: Gwamnatin Kano za ta tantance ma’aikata

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar Kano ta umarci dukkan ma’aikatan jihar da su gabatar da kawunansu domin tantancesu gabanin biyansu albashin watan Maris .

Kadaura24 ta rawaito Sakataren gwamnatin jihar Alhaji Ibrahim Faruk ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishin sa ranar Litinin.

Ya bayyana cewa an dauki matakin domin magance yawan korafe-korafen da ma’aikatan suka yi na samun matsalolin a albashinsu na watan Janairu da Fabrairu.

InShot 20250309 102403344
Talla

“Za a kafe Sunayen ma’aikatan da ake biya albashi a ma’aikatu da hukumomin jihar da ma sakatariyar kananan hukumomi 44 na jihar don sauƙaƙe aikin,” in ji Faruk.

Ya kara da cewa an umurci ma’aikatan da su je ma’aikatunsu don mika sunayensu tare da kai rahoton duk wata matsala da suka samu domin daukar matakin gaggawa.

Domin sa ido kan aikin tantancewar gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin shugaban ma’aikata Alhaji Abdullahi Musa. A cewar Faruk, “An bukaci kwamitin da ya gaggauta aiwatar da aikin domin baiwa gwamnati damar biyan albashin watan Maris a daidai lokacin da ya kamata.”

Yanzu-yanzu: EFCC ta bayyana dalilan da su ka sa ta kama Jarumar Tiktok Murja Kunya

Ya kuma bai wa ma’aikatan tabbacin cewa aikin tantance war ba zai kawo cikas ga ayyukan gwamnati a ma’aikatu da sakatariyoyin kananan hukumomi ba, saboda an dauki matakan da za su hana hakan.

Yayin da bikin Eid-el-Fitr ke gabatowa, Faruk ya jaddada aniyar gwamnati na ganin an biya albashi kafin sallah.

Sakataren gwamnatin Kano ya bukaci ma’aikatan gwamnatin da su baiwa wadanda za su yi aikin tantancewar hadin kai don su kammala aikin cikin nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Matatar Dangote ta dakatar da sayar da fetur a Naira

Matatar Dangote ta sanar da dakatar da sayar da...

Neman Kudi na zo Kannywood ba fadakarwa ba – Sadiq Sani Sadiq

    Fitaccen jarumi a Masana’antar Kannywood Sadik Sani Sadik ya...

Hatsari Guda Biyu da Su ka Canza Rayuwar Matashi Nuraddin, Amma ba su Dakushe Burinsa ba

Nuraddin ya fuskanci manyan jarabawa guda biyu a rayuwar...

Zargin Handama: Al’ummar Garin Danzaki Sun Nemi Agajin Gwamnan Kano

Daga Rabi'u Usman   Al'ummar garin Danzaki sun koka da yadda...