Muhimmin Sakon Murtala Sule Garo ga Al’ummar Jihar Kano

Date:

 

Assalamu alaikum wa Rahmatullah

Ina mika sakon gaisuwa a yayin da al’ummar Musulmi a Najeriya da sauran sassan duniya daban-daban su ka fara gudanar da azumin watan Ramadan.

Tabbas wannan babbar dama ce a garemu ta inganta alakarmu da Allah maɗaukakin sarki ta hanyar habaka ibadarmu da neman yafiyarsa.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ina amfani da wannan dama wajen kira ga al’ummar musulmi dan yin koyi da dabi’un annabin rahama amincin Allah ya tabbata a gareshi wajen nuna tausayi da jinkai da karamci da kuma taimakawa marasa karfi.

Wannan wata mai alfarma dama ce ta tunawa da marasa karfi a cikinmu tun daga ‘yan uwa da makwafta har izuwa sauran al’umma.

Shekarau ya magantu kan batun sake hadewarsu da Kwankwaso

Hakazalika ina kira ga al’ummar jihar Kano da su dukufa wajen addu’o’in zaman lafiya da cigaba da yalwar arziki.

Ina yi wa kowa fatan alkairi. Allah ya karbi ibadinmu ya kuma sa mu kasance cikin bayin da zai yanta. Amin

Ramadan Kareem, Jumu’at Mubarak!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

  Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin...

Cikakken Bayani Kan Yan Bindigar da Yansanda Su Ka Kama a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar...

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gidauniyar Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa...

Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da...