Fyade: Kotu ta yankewa wasu mutane 3 hukuncin kisa da yanke musu Mazakuta

Date:

 

 

An yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya da kuma yanke mazakuta (Dandatsa) ga wasu mutum uku da aka bayyana sunayensu da John Moses, Yakubu Mohammed da Mustapha Musa, bayan kotu ta same su da laifin fyade a Kaduna.

LEADERSHIP ta rawaito cewa kwamishiniyar Ma’aikatar Kula da Harkokin Jin Kai da Ci gaban Al’umma ta Jihar Kaduna, Hajiya Rabi Salisu, ce ta bayyana hakan a Kaduna a jiya Laraba.

InShot 20250115 195118875
Talla

A cewar Kwamishiniyar, wacce ke da jajircewa wajen yaki da fyade da duk wani nau’in cin zarafin mata a jihar, ma’aikatar ta samu nasarar gurfanar da mutum uku da aka yanke musu hukunci kan laifin fyade daga watan Yuni 2024 zuwa watan Fabrairu 2025.

An sake samu tsaiko a shari’ar neman a hana kananan hukumomin Kano kudadensu

Ta bayyana hukuncin da aka yankewa mutanen a matsayin ci gaba mai kyau, kuma hakan zai zama izina ga wasu masu aikata irin wannan mugun aiki.

20250228 181700

“Ma’aikatar ta samu hukunci a ranar 7 ga watan Yuni 2024 a gaban Mai Shari’a Nana a shari’a mai lamba KDH/KAD/57c/2023; a shari’a tsakanin Jihar Kaduna Da John Moses, inda aka same shi da laifin fyade da zina da ‘yar cikinsa, karkashin sashe na 258 (1) na kundin dokokin Penal Code na shekarar 2017 da aka gyara, sannan aka yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya da yanke mazakuta.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

2027: Atiku Abubakar ya bayyana matsayarsa game da kasancewarsa a PDP

  Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya musanta rahotannin...

Cikakken Bayani Kan Yan Bindigar da Yansanda Su Ka Kama a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar yansanda ta kasa reshen jihar...

Gidauniyar Sheikh Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa magidanta 600 kayan abinchi a Kano

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gidauniyar Dr. Muhajihid Aminudden ta rabawa...

Gwamna Abba Gida-gida Ya Kaddamar Da Gyaran Hanyoyi 17 A Babban Birnin Kano

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ƙaddamar da...