ICAN ta Fara wayar da Kan Daliban Sakandare muhimmancin Akanta, da Kuma tallafa musu

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Kungiyar kwararrun akantoci ta kasa reshen jihar Kano ta bukaci daliban dake Shirin zana jarrabawar  kammala sikandire da su hada hannu da kungiyar domin tallafa musu don Zama kwararrun akantoci.

 Shugaban kungiyar Abdullahi S Shehu ne ya bayyana hakan yayin da kungiyar ta ziyarci makarantar Tangaza dake kan titin Jami’ar Bayero domin wayar da kan dalibai a game da ayyukann kungiyar da Kuma tallafa musu da kayan karatu.
Malam Abdullahi Shehu yace  Samar da kwararrun akantoci daga tushe shi ne zai tallafa wajan   bunkasa rayuwar al’umma da Kuma basu damar dogaro da kawunansu ba tare da jiran aiki daga gwamnati ba .
 Shima Anasa jawabin Shugaban kungiyar kwararrun akantoci ta kasa reshen Kano da jigawa Dr . Abubakar Umar Faruk ya bayyana cewa dukkanin harkokin rayuwa na yau da kullum suna bukatar gudunmawar kwararrun akantoci, a don haka ya bukaci dalibai dasu hada hannu da kungiyar domin  ganin sun cimma burinsu na rayuwa .
Kungiyar ta bada tallafin kayan karatu ga makaranatar.
Da yake jawabin shugaban makarantar Tangaza Dr Bien ya yabawa kungiyar kwararrun akantoci ta kasa bisa zabar makarantarsu da suka yi domin basu tallafin kayan karatu da Kuma wayar da kan dalibai game da ayyukann kungiyar.
 Wakilin Kadaura24 ya bamu labarin cewa taron ya samu halarta Al’ummar da dama, inda daga bisani kungiyar ta Kai ziyat makaranatar Al-Amin dake unguwar Tal’udu domin mika tallafi da wayar dakan dalibai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...