ICAN ta Fara wayar da Kan Daliban Sakandare muhimmancin Akanta, da Kuma tallafa musu

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Kungiyar kwararrun akantoci ta kasa reshen jihar Kano ta bukaci daliban dake Shirin zana jarrabawar  kammala sikandire da su hada hannu da kungiyar domin tallafa musu don Zama kwararrun akantoci.

 Shugaban kungiyar Abdullahi S Shehu ne ya bayyana hakan yayin da kungiyar ta ziyarci makarantar Tangaza dake kan titin Jami’ar Bayero domin wayar da kan dalibai a game da ayyukann kungiyar da Kuma tallafa musu da kayan karatu.
Malam Abdullahi Shehu yace  Samar da kwararrun akantoci daga tushe shi ne zai tallafa wajan   bunkasa rayuwar al’umma da Kuma basu damar dogaro da kawunansu ba tare da jiran aiki daga gwamnati ba .
 Shima Anasa jawabin Shugaban kungiyar kwararrun akantoci ta kasa reshen Kano da jigawa Dr . Abubakar Umar Faruk ya bayyana cewa dukkanin harkokin rayuwa na yau da kullum suna bukatar gudunmawar kwararrun akantoci, a don haka ya bukaci dalibai dasu hada hannu da kungiyar domin  ganin sun cimma burinsu na rayuwa .
Kungiyar ta bada tallafin kayan karatu ga makaranatar.
Da yake jawabin shugaban makarantar Tangaza Dr Bien ya yabawa kungiyar kwararrun akantoci ta kasa bisa zabar makarantarsu da suka yi domin basu tallafin kayan karatu da Kuma wayar da kan dalibai game da ayyukann kungiyar.
 Wakilin Kadaura24 ya bamu labarin cewa taron ya samu halarta Al’ummar da dama, inda daga bisani kungiyar ta Kai ziyat makaranatar Al-Amin dake unguwar Tal’udu domin mika tallafi da wayar dakan dalibai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...