Gwamnan Kano ya lashe lambar yabo ta gwamna mafi ƙwazo a Afirka

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya kashe lambar yabo ta “Gwarzon Gwamna na Afirka na Shekara” a fannin kyakkyawan shugabanci a bikin bayar da lambobin yabo Karo 14 na mujallar African Leadership Magazine (ALM) da aka gudanar a Casablanca, Morocco.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin, ya fitar a madadin wasu masu taimaka wa shugabannin Afirka da suka halarci taron a Otal din Marriot, Casablanca.

InShot 20250115 195118875
Talla

Wannan girmamawa ta nuna irin nagartar shugabancin Gwamna Yusuf wajen inganta gaskiya, adalci da shugabanci na kowa da kowa, acewar sanarwar.

Acewar Sanusi, Bature, sauye-sauyen da gwamnatinsa ta kawo a fannin ilimi, gine-gine, kiwon lafiya, da bunkasa tattalin arziki sun sanya Jihar Kano zama abin koyi wajen kyakkyawan shugabanci a Afirka.

Rikicin APC: Abdullahi Abbas ya mayarwa da Minista Abdullahi Ata Martani

Gwamnan ya samu wakilcin mai ba shi shawara kan harkokin jiha, Alhaji Usman Bala, wanda tsohon shugaban ma’aikata ne. Gwamnan ya mika wannan lambar yabo ga al’ummar Kano, yana jaddada rawar da suka taka wajen cimma nasarorin da gwamnatin ke samu.

A cewar mujallar African Leadership Magazine, a karkashin jagorancin Gwamna Yusuf, Kano ta samu manyan nasarori ciki har da ware fiye da kashi 31% na kasafin kudin jihar ga fannin ilimi, tallafa wa dalibai masu karatun digiri na biyu a kasashen waje, da kuma amfani da fasahar zamani wajen gudanar da mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...