Gwamnan Yusuf ya yi alkawarin kammala aiyukan da Ganduje ya yi watsi da su a jami’ar Wudil

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ya alkawarin kammala dukkanin aiyukan da tsohuwar gwamnatin Ganduje ta yi watsi da su a jami’ar Kimiya ta Aliko Dangote dake karamar hukumar Wudil.

Gwamna Yusuf ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci jami’ar domin ganin halin da jami’ar take ciki.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa Kadaura24 ya ya ce gwamnan ya zagaya jami’ar bisa rakiyar shugaban jami’ar Musa Tukur Yakasai.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya yiwa dalibai da malaman jami’ar alkawarin kammala dukkanin aiyukan da ba a kammala su, inda ya ce jami’ar ta na da matukar amfani ga al’ummar jihar Kano da ma kasa baki daya.

” Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya samar da Wannan jami’a tun a Zangon mulkinsa na farko, kuma jami’ar ta yaye inginiyoyi daga fannoni daban-daban, don haka dole mu sake zage damtse wajen inganta ta”.

Kwanaki 100: Shugaban karamar hukumar Wudil ya kaddamar da wasu aiyukan raya kasa

Sanarwar ta ce a kokarinsa na bunkasa jami’ar ta Wudil, gwamna Abba Kabir Yusuf ya kara baiwa jami’ar fili kadada 100, wanda jami’ar za ta yi amfani da shi wajen samar da sabuwar tsangayar koyar da harkokin inginiya da kuma gini majalisar kolin jami’ar.

Ya kuma kara da cewa gwamnatinsa tana baiwa Ilimi fifiko ne saboda shi ne ginshikin rayuwar duk wata al’umma .

A jawabinsa shugaban jami’ar ta Aliko Dangote dake Wudil Farfesa Musa Tukur Yakasai ya roki gwamnan da ya gaggauta biyan diyyar masu filaye a kusa da jami’ar domin samun damar yin aikin akan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...