Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu, ya bukaci shugabar kungiyar taurarin Arewa, Hajiya Naja’atu Muhammad, da ta fito fili ta nemi afuwarsa saboda da sharrin da ta yi masa a wani bidiyo da aka wallafa a dandalin Tik Tok .

A cikin faifan bidiyon da aka sanya a Tiktok, Hajia Muhammad ta zargi mai baiwa Shugaba Bola Tinubu shawara akan harkokin tsaro, lokacin yana shugaban hukumar EFCC ya ce Tinubu yana cikin manyan barayin dukiyoyin al’umma .

A wata wasika ta hannun lauyansa, Dr. Ahmed Raji, SAN, Nuhu Ribado, ya ce a bainar jama’a ko a boye, bai taba raya irin wannan maganar a ransa ba.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce kalaman da Hajiya Naja ta yi sun jawo masa matsalar da bai san adadinta ba.

A cikin wasiƙar mai kwanan watan Fabrairu 4, 2025, kuma Dokta Raji yace dole ne Hajiya Naja ta fito ta bayyana hujjojinta, ko kuma ta fito ta janye kalaman nata tare da neman afuwarsa Nuhu Ribado.

Wasikar ta ce “Kalaman sun sanya ana kallon NSA a matsayin wani matum mai magana biyu ko fuska biyu, kuma hakan ya jawo masa matsaloli a gare shi .

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

“Mun baki kwanaki 7 daga ranar da wannan wasika ta same ki, da ki fito manyan jaridun Nigeria guda 5 domin ba da hakuri ga Nuhu Ribado ko kuma mu hadu da ke a gaban Kotu”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...