Yanzu-yanzu: Dangote ya karya farashin man fetur

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Matatar mai ta Dangote ta karya farashin man fetur daga Naira 950 zuwa Naira 890 kan kowace lita a yammacin wannan Asabar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban sashin yada labarai da hulda da jama’a na kamfanin Anthony Chiejina ya sanyawa hannu, kuma aka rabawa manema labarai.

InShot 20250115 195118875
Talla

Sanarwar da matatar man ta Dangote ta fitar ta ce sabon farashin zai soma aiki ne daga yammacin wannan Asabar.

Babban Dalilin da ya sa na Shiga Siyasa – Sani Danja

Sanarwar ta ce kamfanin ya rage farashin man ne sakamakon yadda aka sami saukin makamashi a kasuwar duniya, da kuma yadda farashin danyan mai ya sauka.

Kamfanin ya bukaci yan kasuwar dake sayan kayansu da su tabbatar sun rage farashin don al’umman Nigeria su amfana da saukin domin inganta rayuwarsu kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu yake fata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...