Gwamnatin Kano Za Ta Fara Shirin Yiwa Ali Madakin Gini Kiranye

Date:

Kwamishinan yada labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya ce zai jagoranci yiwa dan majalisarsu na tarayya Hon. Ali Sani Madakin Gini kiranye daga Majalisar , sakamakon al’ummar karamar Hukumar Dala da Kano basa bukatar wakilcinsa.

Kadaura24 ta rawaito Kwamared Waiya ya bayyana haka ne yayin taron masu ruwa da tsaki na karamar Hukumar Dala da Yan jamiyyar NNPP, Wanda aka gudanar a dakin taro na Mumbayya dake nan Kano.

InShot 20250115 195118875
Talla

Ya ce karamar Hukumar Dala tana bukatar jagora jajirtacce Wanda zai Kai matsalolin al’ummar yakin Majalisar wakilai domin a magance su.

Kaso 9.6% na daliban firamare a Kano suka iya karatu – UNICEF

Kwamishinan ya kuma godewa Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bisa tarin mukaman da ya baiwa wadanda suka fito daga karamar hukumar Dala.

Taron ya samu halartar Shugabannin jam’iyyar NNPP na karamar Hukumar Dala da sauran masu ruwa da tsaki na tafiyar Kwankwasiyya a karamar hukumar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...