A karon farko bayan cire shi daga sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya Koka da yadda ya baiwa jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya kuma suka ci amanarsa.

“Alhamdulillah na gama aiki lafiya, Amma dai Allah ya hada mu da mutane marasa amana, mun ba da gudunmawa daidai gwargwado, Amma an ci amanarmu, Ina baku hakuri ku jira lokaci zai yi da zamu fito da maganganu sala-sala”.

Dr. Baffa Bichi ya bayyana hakan ne lokacin da wasu matasa maza da mata suka taro shi bayan ya dawo daga kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umara.

Talla

Ya ce yanzu ba lokacin magana ba ne, amma idan lokacin yayi matasan za su ji bayanai kala-kala.

” Na gode muku, Ina kuma ba ku hakuri, yanzu ba lokacin magana ba ne, amma muna da maganganu a rubuce muna da su Audio da Bidiyo idan lokacin ya yi za mu fito da su sala-sala”. Inji Baffa Bichi

Dr. Baffa Bichi ya ce zai fito ya fadawa duniya rashin amanar da aka yi masa don gudun kada a kara basu amana, inda ya kira su da masu fadar amana a baki amma kuma ba su da ita a aikace.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...