A karon farko bayan cire shi daga sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya Koka da yadda ya baiwa jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya kuma suka ci amanarsa.

“Alhamdulillah na gama aiki lafiya, Amma dai Allah ya hada mu da mutane marasa amana, mun ba da gudunmawa daidai gwargwado, Amma an ci amanarmu, Ina baku hakuri ku jira lokaci zai yi da zamu fito da maganganu sala-sala”.

Dr. Baffa Bichi ya bayyana hakan ne lokacin da wasu matasa maza da mata suka taro shi bayan ya dawo daga kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umara.

Talla

Ya ce yanzu ba lokacin magana ba ne, amma idan lokacin yayi matasan za su ji bayanai kala-kala.

” Na gode muku, Ina kuma ba ku hakuri, yanzu ba lokacin magana ba ne, amma muna da maganganu a rubuce muna da su Audio da Bidiyo idan lokacin ya yi za mu fito da su sala-sala”. Inji Baffa Bichi

Dr. Baffa Bichi ya ce zai fito ya fadawa duniya rashin amanar da aka yi masa don gudun kada a kara basu amana, inda ya kira su da masu fadar amana a baki amma kuma ba su da ita a aikace.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...