A karon farko bayan cire shi daga sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya Koka da yadda ya baiwa jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya kuma suka ci amanarsa.

“Alhamdulillah na gama aiki lafiya, Amma dai Allah ya hada mu da mutane marasa amana, mun ba da gudunmawa daidai gwargwado, Amma an ci amanarmu, Ina baku hakuri ku jira lokaci zai yi da zamu fito da maganganu sala-sala”.

Dr. Baffa Bichi ya bayyana hakan ne lokacin da wasu matasa maza da mata suka taro shi bayan ya dawo daga kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umara.

Talla

Ya ce yanzu ba lokacin magana ba ne, amma idan lokacin yayi matasan za su ji bayanai kala-kala.

” Na gode muku, Ina kuma ba ku hakuri, yanzu ba lokacin magana ba ne, amma muna da maganganu a rubuce muna da su Audio da Bidiyo idan lokacin ya yi za mu fito da su sala-sala”. Inji Baffa Bichi

Dr. Baffa Bichi ya ce zai fito ya fadawa duniya rashin amanar da aka yi masa don gudun kada a kara basu amana, inda ya kira su da masu fadar amana a baki amma kuma ba su da ita a aikace.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...