Tsarin Manchester United bai dace da ni ba – Zidane

Date:

Yunƙurin Manchester United na ɗauko Zinedine Zidane ya gamu da cikas, inda wasu majiyoyi na kusa da tsohon kocin Real Madrid ya ce ba ya sha’awar zuwa Old Trafford.

A ranar Asabar Manchester United ta raba gari da Ole Gunner Soskjear bayan kashin da da ƙungiyar ta sha hannuin Watford 4-1.

A watan Mayun bana Zidane a bar Real Madrid a matsayin kocinta karo na biyu.

Ya lashe kofin zakarun turai a Madrid sau uku a jere daga 2016.

Bayan ya bar ƙungiyar a 2018, ya sake dawo wa daga baya inda kuma ya lashe kofin La Liga da Super Cup a 2020.

Majiyoyin da ke kusa da tsohon ɗan wasan na Faransa sun ce Zidane wanda yanzu ba shi da ƙungiya ba ya da sha’awar aikin horar da Manchester United.

An alaƙanta shi da ƙungiyar Paris St-Germain ta Faransa, kuma zai fi maraba da buƙatar idan har ta samu.

  1. Mauricio Pochettino, wanda aka fi maganarsa a matsayin wanda zai zama kocin Manchester,yanzu shi ne mai horar da PSG kuma ana tunanin Zidane zai iya maye gurbinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...