Tsarin Manchester United bai dace da ni ba – Zidane

Date:

Yunƙurin Manchester United na ɗauko Zinedine Zidane ya gamu da cikas, inda wasu majiyoyi na kusa da tsohon kocin Real Madrid ya ce ba ya sha’awar zuwa Old Trafford.

A ranar Asabar Manchester United ta raba gari da Ole Gunner Soskjear bayan kashin da da ƙungiyar ta sha hannuin Watford 4-1.

A watan Mayun bana Zidane a bar Real Madrid a matsayin kocinta karo na biyu.

Ya lashe kofin zakarun turai a Madrid sau uku a jere daga 2016.

Bayan ya bar ƙungiyar a 2018, ya sake dawo wa daga baya inda kuma ya lashe kofin La Liga da Super Cup a 2020.

Majiyoyin da ke kusa da tsohon ɗan wasan na Faransa sun ce Zidane wanda yanzu ba shi da ƙungiya ba ya da sha’awar aikin horar da Manchester United.

An alaƙanta shi da ƙungiyar Paris St-Germain ta Faransa, kuma zai fi maraba da buƙatar idan har ta samu.

  1. Mauricio Pochettino, wanda aka fi maganarsa a matsayin wanda zai zama kocin Manchester,yanzu shi ne mai horar da PSG kuma ana tunanin Zidane zai iya maye gurbinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...