Cigaban al’umma:Kungiyar NNPP New Media ta karrama shugaban karamar hukumar Gwarzo

Date:

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo

Shugaban Kungiyar NNPP New Madia na jihar kano Comd. Salman Ibrahim Muhammad yace sun karrama shugaban karamar hukumar Gwarzo ne saboda kokarin da yake yi domin kawo cigaba ga al’ummar yankin.

Comd. Salman ya kara da cewa zasu cigaba da sanya idanu akan ayyukan da shugabannin kananan Hukumomi 44 daka jihar kano suke yi domin su basu lambar girmamawa wanda hakan na kara zaburar da shuwagabanin wajen cigaba da ayyukan Alkairi ga al’ummar da suke shugabanta.

Ya kuma ce shugaban karamar Hukumar Gwarzo shi ne na farko da su ka fara karramawa saboda tun yana shugaban riko yake aikace-aikacen bunkasa jama’a la’akari da hakan yasa suka fara da shi.

Talla

A nasa jawabin bayan karramashi a ofishinsa dake sakatariyar Gwarzon a ranar talata, shugaban karamar Hukumar Dr. Mani Tsoho ya bayyana farin cikinsa da wannan karramawa, tare da bayyana yadda suke fadi tashi wajen kawo cigaban da zai amfani al’umma ta fuskar ba da tallafin karatu ga Dalibai.

Kwankwaso ya taya Ganduje Murnar Cika shekaru 75

Ya kara da cewa wannan karamawa da aka yi masa tasa zai kara kaimi tare da shan alwashin cigaba da ayyuka daban-daban, kuma a shirye su ke su yi tafiya kafada da kafada da irin wadannan kungiyoyi domin kawo ciga a fadin jihar kano

Daga karshe ya yabawa gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da mataimakinsa cormd Aminu Abdussalam Gwarzo a bisa yadda suke basu dama bisa yadda suke sahale musu idan suka kai koken wata matsala data addabi Alumma karamar Hukumar Gwarzo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...