Kwankwaso ya taya Ganduje Murnar Cika shekaru 75

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babban Daraktan harkokin Kuɗi na hukumar raya kogunan Hadejia -Jama’ar Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso ya taya Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje murnar cikarsa shekaru 75 da haihuwa.

” Tabbas Dimokaradiyyar Nigeria zata dade tana amfana da irin gudunmawar da Ganduje ya bayar wajen dorewarta, don haka muke alfahari da shi”.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana hakan ne cikin Sakonsa na taya Ganduje murna wanda ya aikowa Kadaura24.

Talla

“A matsayinsa na shugaban jam’iyyarmu ta APC na ƙasa, Ganduje ya hada kan yan jam’iyyar a fadin ƙasar nan, wanda hakan yasa jam’iyyar take samun nasarori a zabukan cike gurbi da aka yi a ƙasar”. Inji Dr Musa Iliyasu

Babban Daraktan Kuɗi na hukumar raya kogunan Hadejia -Jama’ar ya ce a madadinsa da iyalansa da magoya bayansa yana taya Dr. Abdullahi Umar Ganduje murnar zagayowar ranar da aka haife shi.

Adadin Tafiye-tafiyen da Tinubu ya yi a shekarar 2024

” Muna addu’ar Allah ya kara masa lafiya da kwarin gwiwar cigaba da hidimtawa dimokaradiyyar Nigeria, da kuma ciyar da jam’iyyarmu ta APC gaba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...