EFCC ta gurfanar da wanda ake da zargi da almundahanar taki a Kano

Date:

Hukumar EFCC ta gabatar da wani mutum mai suna Sanusi Hashim bisa zargin almundahanar taki ta naira miliyan 108.

An gabatar da Hashim ne a babbar kotun tarayya da ke Zaria a gaban Mai shari’a Kabiru Dabo kan zargin rashawa, wanda ya saɓa da sashe na 293, wanda kuma ya cancani hukunci a ƙarƙashin sashe 294 na kundin laifuka.

Talla

An zarge shi ne da karɓar naira miliyan 108 daga Ahmad Mohammad Liman da Bashiru Mohammad domin ya kawo musu taki, amma ya ƙi kai musu, zargin da ya ƙaryata.

A ƙarshe Mai shari’a Dabo ya ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 10 ga Fabrairun 2025, sannan ya buƙaci a ajiye wanda ake ƙara a kurkuku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke wa wani hukuncin daurin gidan yari bisa laifin kona tayoyin mota a Kano

Ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi ta jihar Kano ta...

Bayan ficewa daga PDP Dino Melaye ya koma ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawan Najeriya mai wakiltar Kogi ta...

Ƴan Ghana na zanga-zangar neman korar ƴan Nijeriya daga ƙasar

  Zanga-zanga ta ɓarke a Ghana inda ake zargin ƴan...

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...