Ya kamata Gwamnatin tarayya ta da tallafi a Hajjin 2025 – Hukumar Jin dadin alhazan Kano

Date:

Darakta-Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya yi kira ga gwamnatin tarayyar Najeriya da ta duba yiwuwar ba da tallafin aikin hajjin 2025.

Danbappa ya yi wannan roko ne a wata hirar kai tsaye a shirin Barka da Hatsi na gidan rediyon Freedom da safiyar yau.

Talla

Alhaji Lamin Rabi’u ya bayyana cewa kalubalen da ake fama da shi a fannin tattalin arziki a kasar nan ya yi matukar tasiri ga rayuwar ‘yan kasa da dama, wanda hakan ya sa masu niyyar zuwa aikin Hajji ke shan wahala wajen biyan kudin aikin Hajji.

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun hutun kirsimeti da sabuwar shekara

Ya jaddada cewa bayar da tallafin zai saukakawa musulmai wajen samun damar biyan kuɗin sauke farali a bana.

“Bisa la’akari da halin da al’umma su ke ciki, ina kira ga Gwamnatin Tarayya da ta duba yiwuwar bayar da tallafi domin amfanin al’ummar Musulmi. Wannan zai sanya mutane da yawa su sami damar iya biyan kudaden aikin hajjin bana,” in ji shi.

Bugu da kari, Alhaji Lamin Rabi’u ya shawarci dukkan maniyyatan da ke da sha’awar halartar aikin hajjin 2025 da su tabbatar sun biya kudaden ajiya ta hanyar banki kafin cikar wa’adin da aka sanya.

Ya kuma jaddada mahimmancin biyan kudi da wuri domin saukaka tsare-tsare da dabaru na aikin hajji.

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano ta Dukufa wajen ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin bana cikin nasara ga dukkan maniyyatan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...

Majalisar Dokokin Kano ta yi Doka kan masu tufar da yawu da majina a titi

Majalisar Dokokin jihar Kano ta amince da dokar cin...