Yan Jam’iyyar Adawa ne suka dawo da fadan daba Kano – Gwamnan Abba Gida-gida

Date:

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya zargi yan jam’iyyar adawa da kokarin kawo rashin zaman lafiya jihar saboda manufarsu ta siyasa.

” Ganin da suka yi an sami zaman lafiya cigaba na shigowa jihar kano shi yasa marasa kishin jihar kano yan adawa suke kokarin sai sun dukufar da jihar ta koma baya, to Muna fada musu ba za mu lamunci hakan ba”.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin taron majalisar zartarwa ta jihar da ya jagoranta a wannan rana ta laraba.

Talla

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24, ya ce gwamnan ya ce binciken jami’an tsaro ya tabbatar da cewa yan jam’iyyar adawa ne suka haifar da fadan daban da akwai kwananan a Kano.

Ya ce gwamnatin jihar kano ba zata lamunci wannan Mummunar dabi’ar ba, zata dauki tsauraran matakai domin ganin an yi maganin duk wanda ya sake haifar da rashin zaman lafiya a jihar Kano.

” Za mu cigaba da aiki da hukumomin tsaro dake aiki a jihar kano domin tabbatar da zaman lafiyar jihar, da kuma magance duk wani yunkuri na haifar da rashin zaman lafiya a wannan jihar ta mu ta Kano”. Inji Gwamna Abba Kabir

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a yan kwanakin nan an sha fama da fadan daba a wasu unguwannin birnin kano, wanda hakan ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...