Bashir Gentile ya Gargaɗi Shugaban Majalisar Wakilai Kan Kudirin Dokar Harajin Tinubu

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Dalibin siyasar duniya, kuma mai sharhi kan al’amuran siyasar Nigeriya Alhaji Bashir Hayatu Gentile, ya bukaci shugaban majalisar wakilan Nigeria Tajudeen Abbas da ya ji tsoron Allah kar ya bari a cutar da al’ummar Arewacin Nigeria, ta hanyar amince da kudirin dokar gyaran haraji da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aika musu.

“Ka sani Allah ne ya baka wannan mukamin da ka ke kai ba Tinubu ko jam’iyyar APC ba, kuma ka tuna kai Dan gidan sarautar Iyan Zazzau ne, don haka kar ka bari ayi amfani da mukamin da Allah ya baka har a zo da wani abu da zai cutar da al’ummar Arewacin Nigeria”.

Bashir Gentile ya bayyana hakan ne cikin wani sakon Murya da ya aikowa Jaridar KADAURA24 a ranar Juma’a.

Talla

Ya ce kudirin harajin da Tinubu ya tura majalisa, idan har ya sami amincewa yan majalisar zai cutar da al’ummar Arewacin Nigeria sosai, don haka ya ce shugaban majalisar ya yiwa Allah da manzonsa Kar ya bari kudirin ya wuce.

” Na tattauna da yan majalisar tarayya na arewa sun kai 187 Amma dukkaninsu sun tabbatar min da cewa kai ne matsala domin ka hura musu wuta sai sun baka goyon bayan kan tabbatar da wannan kudiri na haraji da zai lalata rayuwar wadanda ma ba a haifesu ba, domin zai lalata komai na Arewacin Nigeria”. Inji Bashir Gentile

Za mu tabbatar Yan arewa sun hukunta duk dan majalisar da ya goyi bayan tsarin harajin Tinubu – Falakin Shinkafi

“Ina kara yi maka nasiha mai girma iyan Zazzau ka ji tsoron Allah, domin Allah ya ce duk abun da ka shuka shi zaka jirba walau alheri ko akasin haka, don haka kar ka bari ayi amfani da kai wajen bautar da al’ummar Arewacin Nigeria”.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito al’umma da dama Arewacin Nigeria suna ta sukar wannan kudirin gyaran dokar harajin, wanda masa suka ce zai gurgunta tattalin arzikin Arewacin Nigeria baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...