Yanzu-Yanzu: An kashe Dan ta’addan da ya shirya Sace Daliban Makarantar Kankara ta jihar Katsina

Date:

Rahotonni sun tabbatar da cewa fitaccen dan ta’addan da ya shirya sace ‘Yan Makarantar Kankara a cikin jihar Katsina, Auwalun Daudawa an kashe shi.
 Wannan na zuwa kwanaki kadan bayan ya koma daji.


 Kwamishanan tsaron harkokin cikin gida na jihar Zamfara, Abubakar Justice Dauran ne ya tabbatar wa DW Hausa da labarin.


 Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe Daudawa ne da yammacin ranar Juma’a a lokacin da sukai musayar wuta da wasu gungun abokan hamayyarsu a dajin Dumburum da ke tsakanin karamar Hukumar Zurmi a Jihar Zamfara da karamar Hukumar Batsari a Jihar Katsina.


 Shahararren dan fashin nan ya yi kaurin suna bayan da ya kitsa kai hari a Makarantun Sakandaren Gwamnati da ke Kankara inda ya sace sama da ’yan makaranta 300 a cikin dare.
 Watanni biyu bayan haka, dan fashin ya bayyana a Gusau, babban birnin Zamfara, tare da mutanensa biyar inda ya sanar da tubansa tare da mika bindigogin AK guda 20 da wasu makamai ga ‘yan sanda.

2 COMMENTS

  1. Lallai Kadaura na bayar da gagarumar gudunmawa ga makaranta Hausa a Jafar sadarwa zamani.
    Allah ya taimaki Kadaura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yadda kamfanin ganyen shayi na Z&Y ke fuskantar matsin lamba daga TOP TEAA

Wani matashin ɗan kasuwa daga jihar Kano, mai suna...

Gwamnatin Kano ta bayyana sunayen unguwannin da aka sami gurbatacciyar Iska

    Wani rahoto na mako-mako kan yanayin lafiyar iska da...

Sallah: Gwamnatin Kano za ta hukunta gidan wasan da ya bar masu shigar banza da shaye-shaye

Daga Rahama Umar Kwaru   A kokarin ta na yaki da...

Sallah: Hussari ya sauke kabakin arziki ga yan jam’iyyar APC na karamar hukumar Gwale

Daga Ibrahim Abubakar Diso   Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya...