Wata Kungiya a Kano ta koyawa marayu 300 sana’o’in hannu da haddar Al-Qur’ani

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Wata Kungiya dake tallafawa a jihar kano mai suna Kano Network for Orphans and human development ta samu nasarar horas da marayu 300 sana’o’in hannu da koyar da su haddar Al-Qur’ani a wani bangare na ganin ta inganta rayuwar marayu a jihar.

An horar da marayun ne waɗannan sana’o’i da haddar al’qur’anin da nufin kyautata halayensu da dabi’unsu don samu zamo masu mutane na gari da al’umma za su yi alfahari da su.

A jawabinsa na maraba shugaban kungiyar Kwamared Adam Umar ya bayyana cewa tallafawa marayu yana da matukar mahimmancin gaske a nan duniya da Kuma gobe kiyama.

Talla

Ya ce, “Suna bukatar sanin Allah Sannan su sami ilimin sana’o’in da zasu iya dogara da kawunansu ta yadda zasu gudanar da kyakykyawar rayuwa”.

Dagacin da ya Shekara 91 yana mulki ya Rasu 

Da yake jawabi a madadin kwamishinan ilimi na jihar Kano, Umar Haruna Doguwa, wanda ya wakilce shi Hon. Habeeb Hassan El-Yakub, mataimaki na musamman ga gwamna kan koyar da sana’o’i ya yaba da kokarin kungiyar na tallafawa shirye-shiryen gwamnati na koyawa matasa sana’o’in hannu.

Ya kuma yi alkawarin cewa nan ba da dadewa ba gwamnatin jihar za ta samar da cibiyoyin koyar da sana’o’in hannu a dukkanin kananan hukumomin jihar Kano 44, sannan ya yi alkawarin tallafa wa kungiyar domin ta gina matsuguninta na din-din-din.

Mai Martaba Sarkin Rano, Ambasada Dr. Muhammad Isa Umaru wanda Wazirin Rano ya wakilta, Mal. Kabiru Sani, ya yabawa kungiyar Marayu da cigaban bil Adama ta Kano bisa jajircewarta na tallafawa marayun.

A yayin taron an kuma karrama mutanen da suka bayar da gudunmawa sosai wajen jin dadin marayu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...