Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo Ya Bada Tallafin Bas Mai Kujeru 60 Ga Jami’ar FUDMA

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA) ta gudanar da taron yaye ɗalibai a karo na 9, a inda ta samu wani karamcin kyauta ta musamman daga Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, a inda ya bai wa jami’ar motar bas mai cin mutum 60.

Sabuwar motar bas ɗin za ta sauƙaƙa ƙalubalen sufuri ga ɗalibai, waɗanda da yawa daga cikinsu ke kokawa bisa ƙarancin motocin zirga-zirga.

A yayin bikin, shugaban jami’ar ta FUDMA, Farfesa Armaya’u Bichi, ya bayyana matuƙar jin daɗin jami’ar ga irin gudunmawar da Farfesa Gwarzo ya bayar.

Talla

“Wannan motar bas ɗin za ta zama babbar ƙadara ga ɗalibanmu, tare da ƙarfafa su wajen halartar azuzuwa da kuma shiga cikin harkokin karatu,” in ji Farfesa Bichi.

“Muna matuƙar godiya da jajircewar Farfesa Gwarzo na tallafawa ilimi a aikace ta hanyoyi masu tasiri.

Martani: Ku daina ƙalubalantar Abdullahi Gwarzo Daga Umar Hamza Gwangwazo

Ɗalibai da ma’aikatan da suka halarci taron sun yi nuna jinɗaɗin su bisa yadda wannan kyautar sabuwar motar bas za ta yi tasiri ga rayuwar su ta tau da kullum a harabar jami’a.

Karamcin na Farfesa Gwarzo abin koyi ne kuma tunatarwa ne mai tasiri ga yadda tallafin zai iya haɓaka ilimi da ba da gudummawa ga nasarar ɗalibai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...