Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo Ya Bada Tallafin Bas Mai Kujeru 60 Ga Jami’ar FUDMA

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA) ta gudanar da taron yaye ɗalibai a karo na 9, a inda ta samu wani karamcin kyauta ta musamman daga Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, a inda ya bai wa jami’ar motar bas mai cin mutum 60.

Sabuwar motar bas ɗin za ta sauƙaƙa ƙalubalen sufuri ga ɗalibai, waɗanda da yawa daga cikinsu ke kokawa bisa ƙarancin motocin zirga-zirga.

A yayin bikin, shugaban jami’ar ta FUDMA, Farfesa Armaya’u Bichi, ya bayyana matuƙar jin daɗin jami’ar ga irin gudunmawar da Farfesa Gwarzo ya bayar.

Talla

“Wannan motar bas ɗin za ta zama babbar ƙadara ga ɗalibanmu, tare da ƙarfafa su wajen halartar azuzuwa da kuma shiga cikin harkokin karatu,” in ji Farfesa Bichi.

“Muna matuƙar godiya da jajircewar Farfesa Gwarzo na tallafawa ilimi a aikace ta hanyoyi masu tasiri.

Martani: Ku daina ƙalubalantar Abdullahi Gwarzo Daga Umar Hamza Gwangwazo

Ɗalibai da ma’aikatan da suka halarci taron sun yi nuna jinɗaɗin su bisa yadda wannan kyautar sabuwar motar bas za ta yi tasiri ga rayuwar su ta tau da kullum a harabar jami’a.

Karamcin na Farfesa Gwarzo abin koyi ne kuma tunatarwa ne mai tasiri ga yadda tallafin zai iya haɓaka ilimi da ba da gudummawa ga nasarar ɗalibai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...